1 “Na yi alkawari da idanuna,Me zai sa in ƙyafaci budurwa?
2 Wane rabo zan samu daga wurin Allah a Sama?Wane gādo kuma zan samu daga wurin Mai Iko Dukka a can samaniya?
3 Yakan aika da masifa da lalacewaGa waɗanda suke aikata abin da ba daidai ba.
4 Allah ya san dukan abin da nake yi,Yana ƙididdige dukan takawata.
5 “Idan ina tafiya da rashin gaskiya,Ina hanzari don in aikata yaudara,
6 Bari Allah ya auna ni da ma'aunin da yake daidai,Zai kuwa san mutuncina.
7 Idan dai na kauce daga hanya,Ko kuwa zuciyata ta bi sha'awar idanuna,Idan akwai ko ɗan sofane a hannuna,