20 Idan a zuciyarsa bai sa mini albarka ba,Ko bai ji ɗumi da ulun tumakina ba,
21 Ko na ɗaga hannuna don in cuci maraya,Don na ga ina da kafar kuɓuta,
22 To, ka sa kafaɗuna su ɓaɓɓalle daga inda suke.Ka kakkarya gwiwoyin hannuna.
23 Gama bala'i daga wurin Allah ya razanar da ni,Saboda ɗaukakarsa ba zan iya yin kome ba.
24 “Idan na ce ga zinariya na dogara, ko zinariya tsantsa ita ce jigona,
25 Idan kuma saboda yawan dukiyata nake fariya,Ko saboda abin da na mallaka ne,
26 Idan ga hasken rana nake zuba ido,Ko ga hasken farin wata ne,