19 “Akan hori mutum da cuta mai zafi a gadonsa,Ya yi ta fama da azaba a cikin ƙasusuwansa,
20 Ransa yana ƙyamar abinci,Yana ƙyamarsa kome daɗinsa kuwa.
21 Yakan rame ƙangayau, ƙasusuwansa duk a waje.
22 Yana gab da shiga kabari,Ransa yana hannun mala'ikun mutuwa.
23 “Da a ce akwai wani mala'ika mai sulhuntawa a tsakani,Ko da ɗaya daga cikin dubu ne wanda zai faɗa wa mutum,
24 Mala'ikan da zai yi masa alheri ya ce,‘Ka cece shi daga gangarawa zuwa cikin kabari,Na sami abin da zai fanshe shi!’
25 Naman jikinsa zai koma kamar na saurayi,Zai komo kamar lokacin da yake gaɓar ƙarfinsa.