1 Elihu ya ci gaba da magana.
2 “Ka yi mini haƙuri kaɗan, ni kuwa zan nuna maka,Gama har yanzu ina da abin da zan faɗa in kāre Allah.
3 Zan tattaro ilimina daga nesa,In bayyana adalcin Mahaliccina.
4 Gaskiya nake faɗa ba ƙarya ba,Wanda yake da cikakken sani yana tare da kai.