21 Ka lura kada ka rinjayu a kan aikata mugunta,Gama saboda haka kake shan wannan tsanani,Don a tsare ka daga aikata mugunta.
22 “Duba, Allah Maɗaukaki ne cikin ikonsa,Wa ya iya koyarwa kamarsa?
23 Ba wanda zai iya tsara wa Allah abin da zai yi,Wa ya isa ya ce masa ya yi kuskure?
24 “Ka tuna ka girmama aikinsa,Wanda mutane suke yabo.
25 Dukan mutane sun ga ayyukansa,Sun hango shi daga nesa.
26 Ga shi kuwa, Allah Maɗaukaki ne,Ba mu kuwa san iyakar ɗaukakarsa ba,Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
27 “Allah yakan sa ruwa ya zama tururi,Ya maishe shi ruwan sama,