4 Gaskiya nake faɗa ba ƙarya ba,Wanda yake da cikakken sani yana tare da kai.
5 “Ga shi kuwa, Allah Mai Girma, ba ya raina kowa,Shi mai girma ne, mai cikakkiyar basira.
6 Ba ya rayar da masu laifi,Amma yakan ba waɗanda ake tsananta wa halaliyarsu.
7 Yakan kiyaye waɗanda suke aikata gaskiya,Yakan kafa su har abada tare da sarakuna,A gadon sarauta, ya ɗaukaka su.
8 Amma idan aka ɗaure su da sarƙoƙi,Da kuma igiyar wahala,
9 Sa'an nan yakan sanar da su aikinsuDa laifofin da suke yi na ganganci.
10 Yakan sa su saurari koyarwa,Da umarnai, cewa su juya, su bar mugunta.