22 Tsoro abin dariya ne a gare shi, bai damu ba.Ba ya ba da baya ga takobi,
23 Kibau na ta shillo a kansa,Māsu suna ta gilmawa a gabansa.
24 Da tsananin fushi da hasala yana kartar ƙasa,Da jin ƙarar ƙaho, sai ya yi ta zabura.
25 Sa'ad da aka busa ƙaho yana ce, ‘Madalla.’Yakan ji warin yaƙi daga nesa, da hargowar sarakunan yaƙi da ihunsu.
26 “Ta wurin hikimarka ne shirwa take tashi,Ta buɗe fikafikanta ta nufi kudu?
27 Ta wurin umarninka ne gaggafa take tashi samaTa yi sheƙarta can ƙwanƙoli?
28 A kan dutse take zaune, a can take gidanta,Cikin ruƙuƙin duwatsu.