25 Sa'ad da aka busa ƙaho yana ce, ‘Madalla.’Yakan ji warin yaƙi daga nesa, da hargowar sarakunan yaƙi da ihunsu.
26 “Ta wurin hikimarka ne shirwa take tashi,Ta buɗe fikafikanta ta nufi kudu?
27 Ta wurin umarninka ne gaggafa take tashi samaTa yi sheƙarta can ƙwanƙoli?
28 A kan dutse take zaune, a can take gidanta,Cikin ruƙuƙin duwatsu.
29 Daga can takan tsinkayi abincintaIdanunta sukan hango shi tun daga nesa.
30 'Yayanta sukan tsotsi jini,A inda kisassu suke, can take.”