7 Ai, an haifi mutum domin wahala ne,Tabbatacce ne kamar yadda tartsatsin wuta suke tashi.
8 “In da ni ne kai, da sai in juya wurin Allah,In kai ƙarata a wurinsa.
9 Ba za mu iya fahimtar manyan abubuwa da yake yi ba,Al'ajabansa kuwa ba su da iyaka.
10 Yakan aiko da ruwan sama,Ya shayar da gonaki.
11 I, Allah ne yake ɗaukaka masu tawali'u,Shi yake kuɓutar da dukan waɗanda suke makoki.
12 Yakan birkitar da shirye-shiryen masu wayo.
13 Yakan sa wa masu wayo tarko cikin dabarunsu,Har ba za su yi nasara a dukan abin da suke yi ba.