8 Kuna ganina yanzu, amma ba za ku sāke ganina ba.Idan kuka neme ni, za ku tarar ba na nan.
9 Kamar girgijen da yake bajewa ya tafi,Haka nan mutum yake mutuwa.
10 Ba kuwa zai ƙara komowa ba,Mutanen da suka san shi, duka za su manta da shi.
11 A'a, ko kaɗan ba zan yi shiru ba!Haushi nake ji, zuciyata ta ɓaci,Dole ne in yi magana.
12 “Ya Ubangiji, don me ka sa ni a waƙafi?Kana tsammani ni dodon ruwa ne?
13 Na kwanta ina ƙoƙari in huta,Ina neman taimako don azabar da nake sha.
14 Amma kai kana firgita ni da mafarkai,Kana aiko mini da wahayi da ganegane,