1 Sai Bildad ya yi magana.
2 “Ka gama maganganunka marasa kan gado duka?
3 Allah bai taɓa yin danniya ba,Bai kuma taɓa fāsa aikata abin da yake daidai ba.
4 Lalle 'ya'yanka sun yi wa Allah zunubi,Don haka ya hukunta su yadda ya cancanta.
5 Amma sai ka juyo ka yi roƙo ga Allah Maɗaukaki.