6 Idan kana da tsarki da aminci, Allah zai taimake ka,Ya maido da iyalin gidanka, ya yi maka sakayya.
7 Duk hasarar dukiyan nan da ka yi, ba kome ba neIn aka gwada da abin da Allah zai ba ka nan gaba.
8 “Ka tsai da zuciyarka a kan hikima irin ta zamanin dā.Ka kuma yi ta yin tunani a kan gaskiyar da kakanninmu suka koya.
9 Kwanakinmu 'yan kaɗan ne kawai,Ba mu san kome ba,Mu inuwa ne kawai a fuskar duniya.
10 Amma ka yarda masu hikima na zamanin dā su koya maka,Ka kasa kunne ga abin da za su faɗa.
11 “Iwa ba ta tsirowa inda ba ruwa,Ba a taɓa samunta a ko'ina ba sai a fadama.
12 In ruwan ta ƙafe, ita ce za ta fara bushewa,Tun tana ƙanƙana ba ta isa a yanke a yi amfani da ita ba.