41 Garuruwan da suke cikin yankin ƙasar gādonta ke nan, da Zora, da Eshtawol, da Ir-shemesh,
42 da Shalim, da Ayalon, da Itla,
43 da Elon, da Timna, da Ekron,
44 da Elteki, da Gebbeton, da Ba'alat,
45 da Yahud, da Bene-berak, da Gat-rimmon,
46 da Meyarkon, da Rakkon, tare da karkarar da take gefen Yaffa.
47 Sa'ad da Danawa suka rasa karkararsu, suka tafi, suka yaƙi Leshem. Da suka ci ta, sai suka hallaka mutanenta da takobi, suka mallaki ƙasar, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato Dan.