15 Wanda ya ɗaukar wa baƙo lamuni zai yi da na sani, zai fi maka sauƙi idan ba ruwanka.
16 Mace mai mutunci abar girmamawa ce, amma azzalumai za su sami dukiya.
17 In ka yi alheri, kanka ka samar wa tagomashi, in kuwa ka yi mugunta, kanka ka cutar.
18 A ainihi mugaye ba su cin ribar kome, amma idan ka yi abin da yake daidai, ka tabbata za a sāka maka da alheri.
19 Mutumin da ya yi niyyar aikata abin da yake daidai zai rayu, amma mutumin da ya dukufa ga aikata mugunta zai mutu.
20 Ubangiji yana ƙin masu muguwar niyya, amma yana murna da waɗanda suke aikata abin da yake daidai!
21 Ka tabbata fa za a hukunta mugaye, amma ba za a hukunta adalai ba.