1 Ɗana, ka koyi abin da nake koya maka, sam kada ka manta da abin da na faɗa maka ka yi.
2 Ka kasa kunne ga abin da yake na hikima, ka yi ƙoƙari ka fahimce shi.
3 I, ka roƙi ilimi da tsinkaya.
4 Ka nema da iyakar ƙoƙarinka kamar yadda za ka nemi azurfa, ko kowace irin ɓoyayyiyar dukiya.
5 Idan ka yi za ka san abin da ake nufi da tsoron Ubangiji. Za ka yi nasara a kan koyon sanin Allah.