5 Idan ka yi za ka san abin da ake nufi da tsoron Ubangiji. Za ka yi nasara a kan koyon sanin Allah.
6 Ubangiji ne yake ba da hikima. Ilimi da fahimi kuwa suna cikin kalmominsa.
7 Shi yake tanada wa adalai taimako da kiyayewa, wato mutane masu aminci.
8 Yakan kiyaye waɗanda suke lura da kyau, ya kiyaye waɗanda suke dogara gare shi.
9 Idan ka kasa kunne gare ni za ka san abin da yake daidai, da abin da yake gaskiya, da abin da yake na kirki. Za ka san abin da za ka yi.
10 Za ka zama mai hikima, iliminka zai faranta maka rai.
11 Tsinkayarka da fahiminka za su tsare ka.