14 Zina tarko ce, takan kama waɗannan waɗanda Ubangiji yake fushi da su.
15 Halin yara ne su yi wauta da waɗansu abubuwa na rashin kula, amma tsumagiya za ta koya musu abin da ya fi kyau.
16 Idan attajirai kake yi wa kyauta, kana kuma zaluntar matalauta don ka arzuta, kai kanka za ka talauce.
17 Ka kasa kunne zan koya maka abin da masu hikima suka faɗa, yi nazari a kan koyarwarsu.
18 Za ka yi murna in ka tuna da su, ka iya faɗarsu.
19 Ina so ka dogara ga Ubangiji, don haka zan faɗa maka su yanzu.
20 Na rubuta maka karin magana, suna ƙunshe da ilimi da kyakkyawar shawara.