11 Ubangiji Mai Iko shi ne kāriyarsu, shi zai yi magana dominsu.
12 Ka mai da hankali ga malaminka, ka koyi dukan abin da kake iyawa.
13 Kada ka bar yaro ba horo, gama ko ka duke shi ba za a kashe shi ba.
14 Lalle ne za ka ceci ransa.
15 Ɗana, idan ka zama mai hikima zan yi murna ƙwarai.
16 Zan yi murna idan na ji kana faɗar magana da hikima.
17 Kada ka yi ƙyashin masu aikata zunubi tsoron Ubangiji kaɗai za ka sa a gaba.