14 Lalle ne za ka ceci ransa.
15 Ɗana, idan ka zama mai hikima zan yi murna ƙwarai.
16 Zan yi murna idan na ji kana faɗar magana da hikima.
17 Kada ka yi ƙyashin masu aikata zunubi tsoron Ubangiji kaɗai za ka sa a gaba.
18 Idan haka ta samu za ka yi farin ciki nan gaba.
19 Ka saurara, ya ɗana, ka zama mai hikima. Ka yi tunani mai zurfi a kan hanyarka.
20 Kada ka zauna da mashayan ruwan inabi, ko masu haɗama.