3 Sa'ad da nake ɗan yaro tilo a wurin iyayena,
4 mahaifina yakan koya mini, yakan ce, “Ka tuna da abin da nake faɗa maka, kada ka manta. Ka yi abin da na faɗa maka za ka rayu.
5 Ka nemi hikima da basira! Kada ka manta ko ka ƙyale abin da na faɗa.
6 Kada ka rabu da hikima, gama za ta kiyaye ka, ka ƙaunace ta, za ta kiyaye lafiyarka.
7 Samun hikima shi ne mafificin abin da za ka yi. Kome za ka samu dai, ka sami basira.
8 Ka ƙaunaci hikima, za ta girmama ka. Ka rungume ta, za ta kawo maka daraja.
9 Za ta zamar maka rawanin daraja.”