1 Ɗana, ka taɓa yin alkawari ka ɗaukar wa wani lamuni?
2 Maganganunka sun taɓa kama ka, ko alkawaranka sun taɓa zamar maka tarko?
3 To, ɗana, kana cikin ikon wannan mutum, amma ga yadda za ka yi ka fita, sheƙa zuwa wurinsa, ka roƙe shi ya sake ka.
4 Kada ka yarda ka yi barci ko ka huta.
5 Ka fita daga cikin tarkon kamar tsuntsu ko barewar da ta tsere wa maharbi.