9 da magariba cikin duhu.
10 Sai ta tarye shi, ta ci ado kamar karuwa, tana shirya yadda za ta yaudare shi.
11 (Ba ta jin tsoro, ba ta kuma jin kunya, ko yaushe tana ta gantali a tituna.
12 Takan tsaya tana jira a kowace kusurwa, wani lokaci a tituna, wani lokaci kuma a kasuwa.)
13 Ta rungumi saurayin, ta sumbace shi, ta dubi tsabar idonsa ta ce,
14 “Na miƙa hadayu yau, ina da nama na hadayu.
15 Shi ya sa na fito ina nemanka, ina so in gan ka, ga shi kuwa, na gan ka!