20 A kan hanyar adalci nake tafiya,Rankai a kan hanyoyin gaskiya.
21 Ina ba da dukiya ga waɗanda suke ƙaunata,Ina kuma cika gidajensu da wadata.
22 “Ni ce halittar farko da UbangijiYa fara halittawa daga cikin ayyukansa tuntuni.
23 Da farkon farawa ni aka fara halittawaKafin a yi duniya.
24 Ni aka fara yi kafin tekuna,A sa'ad da ba maɓuɓɓugan ruwa.
25 Ni aka fara yi kafin a yi duwatsu,Kafin a kafa tuddai a wurarensu,
26 Kafin Allah ya halicci duniya da filayenta,Ko ɗan ɓarɓashin ƙasa.