26 Ubangiji ya yi magana da Musa, cewa,
27 rana ta goma ga watan bakwai za ta zama rana ta yin kafara da lokacin yin muhimmin taro. Kada su ci abinci a ranar, su taru su yi sujada, su miƙa hadaya taƙonawa ga Ubangiji.
28 Ba za su yi aiki a wannan rana ba, gama rana ce ta yin kafara dominsu.
29 Duk wanda ya ci abinci a wannan rana ba za a lasafta shi ɗaya daga cikin jama'ar Allah ba.
30 Duk kuma wanda ya yi aiki a wannan rana, Ubangiji kansa zai kashe shi.
31 Wannan ka'ida ta shafi dukan zuriyarsu a duk inda suke.
32 Daga faɗuwar ranar tara ga watan, har zuwa faɗuwar ranar goma ga watan, su kiyaye wannan ta zama ranar hutu musamman. A wannan lokaci ba wanda zai ci abinci.