3 Mun zama marayu, marasa ubanni,Uwayenmu sun zama kamar matan da mazajensu sun mutu.
4 Dole ne mu biya ruwan da za mu sha,Dole ne kuma mu sayi itace.
5 Masu binmu a ƙyeyarmu suke, suna korarmu da zafi,Mun gaji, ba a yarda mu huta.
6 Mun miƙa hannu ga Masar da AssuriyaDon mu sami abinci.
7 Ubanninmu sun yi zunubi, ga shi kuwa, ba su,Mu kuwa muna ɗaukar alhakin muguntarsu.
8 Bayi suke mulkinmu,Ba kuwa wanda zai cece mu daga hannunsu.
9 Sai mun yi kasai da ranmu kafin mu sami abinci,Domin akwai masu kisa a jeji.