27 Ku mutanen Isra'ila, za ku sani inacikinku,Ni ne kuwa Ubangiji Allahnku, bawani kuma,Ba kuma za a ƙara kunyatar damutanena ba.”
28 “Bayan wannan zan zubo Ruhuna akan jama'a duka,'Ya'yanku mata da maza za su iyarda saƙona,Tsofaffinku kuwa za su yi mafarkai,Samarinku za su ga wahayi da yawa.
29 A lokacin zan zubo Ruhuna,Har a kan barori mata da maza.
30 “Zan yi faɗakarwa a kan wannanranaA sararin sama da a duniya.Za a ga jini, da wuta, da murtukewarhayaƙi,
31 Rana za ta duhunta,Wata zai zama ja wur kamar jini,Kafin isowar babbar ranan nan maibantsoro ta Ubangiji.