1 Da na ɗaga idona, sai ga wani mutum yana riƙe da igiyar awo.
2 Sai na ce, “Ina za ka?”Ya ce mini, “Zan tafi in auna Urushalima don in san fāɗinta da tsawonta.”
3 Sai ga mala'ikan da yake magana da ni, ya fita, sai wani mala'ika kuma ya zo ya sadu da shi.
4 Ya ce masa, “Ka yi gudu, ka faɗa wa saurayin can, cewa za a zauna a Urushalima kamar a ƙauyuka marasa garu, saboda yawan mutane da dabbobi da suke cikinta.