12 Tun da yake muna da sa zuciya irin wannan, to, muna magana ne gabanmu gaɗi ƙwarai.
13 Ba kamar Musa muke ba, wanda ya rufe fuskarsa da mayafi, don kada Isr'ailawa su ga ƙarewar ɗaukakar nan mai shuɗewa.
14 Amma hankalinsu ya dushe, domin har ya zuwa yau, in ana karatun Tsohon Alkawari, mayafin nan har yanzu ba a yaye yake ba, domin ba ya yayuwa sai ta wurin Almasihu kaɗai.
15 Hakika har ya zuwa yau, duk lokacin da ake karatun littattafan Musa, sai mayafin nan yakan rufe zukatansu.
16 Amma da zarar mutum ya juyo ga Ubangiji, akan yaye masa mayafin.
17 To, Ubangiji fa shi ne Ruhu, a inda Ruhun Ubangiji yake kuma, a nan 'yanci yake.
18 Mu dukanmu kuma, fuskokinmu ba lulluɓi, muna nuna ɗaukakar Ubangiji, kamar madubi, ana sauya mu mu ɗauki kamanninsa cikin ɗaukaka mai hauhawa. Ubangiji kuwa wanda yake ruhu, yana zartar da haka.