1 To, ina so ku san irin yawan shan faman da nake yi dominku, da waɗanda suke a Lawudikiya, da kuma duk waɗanda ba su taɓa ganina ba.
2 Sona a ƙarfafa musu zuciya, ƙauna tana haɗa su, har su sami dukkan mayalwaciyar fahimta tabbatacciya, da sanin asirin nan na Allah, wato Almasihu,
3 wanda shi ne taska, wato maɓoyar dukkan mafifitan hikima da sani.
4 Na faɗi wannan ne don kada kowa ya hilace ku da maganar yaudara.