30 da zarar sun fara toho, kuna gani, ku da kanku kun san damuna ta yi kusa ke nan.
31 Haka kuma sa'ad da kuka ga waɗannan al'amura suna aukuwa, ku sani Mulkin Allah ya gabato.
32 Hakika, ina gaya muku, zamanin nan ba zai shuɗe ba, sai duk abubuwan nan sun auku.
33 Sararin sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za ta shuɗe ba.”
34 “Ku kula da kanku fa, kada zuciyarku ta zarme da yawan shaye-shaye da buguwa, da kuma taraddadin wannan duniya, har ba labari ranan nan ta mamaye ku kamar tarko.
35 Don haka, za ta auka wa mazaunan duniya duk, kowa da kowa.
36 Koyaushe ku zauna a faɗake, kuna addu'a ku sami ikon tsere wa dukan waɗannan al'amura da za su auku, ku kuma tsaya a gaban Ɗan Mutum.”