64 Suka ɗaure masa idanu, suka tambaye shi, suka ce, “Yi annabci! Wa ya buge ka?”
65 Suka kuma yi ta masa baƙaƙen maganganu masu yawa, suna zaginsa.
66 Da gari ya waye sai majalisar shugabannin jama'a ta haɗu, da manyan firistoci da kuma malaman Attaura. Suka kai shi ɗakin majalisarsu suka ce,
67 “To, in kai ne Almasihu, gaya mana.” Amma ya ce musu, “Ko na gaya muku, ba za ku gaskata ba.
68 In kuma na yi muku tambaya, ba za ku mai da jawabi ba.
69 Amma nan gaba, Ɗan Mutum zai zauna dama na Allah Mai iko.”
70 Duk suka ce, “Ashe, kai ɗin nan Ɗan Allah ne?” Sai ya ce musu, “Yadda kuka faɗa, ni ne.”