4 Sai suka tafi, suka tarar da aholakin a ɗaure a ƙofar gida a bakin hanya, suka kwance shi.
5 Sai waɗanda suke tsaitsaye a gun suka ce musu, “Don me kuke kwance aholakin nan?”
6 Suka faɗa musu abin da Yesu ya ce. Su kuwa suka ƙyale su suka tafi.
7 Suka kawo wa Yesu aholakin, suka shimfiɗa mayafansu a kai, ya hau.
8 Sai mutane da yawa suka shisshimfiɗa mayafansu a hanya, waɗansu kuma suka baza ganyen da suka kakkaryo a saura.
9 Da na gaba da na baya suka riƙa sowa suna cewa, “Hosanna! Albarka ta tabbata ga mai zuwa da sunan Ubangiji!
10 Albarka ta tabbata ga mulkin nan mai zuwa na ubanmu Dawuda! Hosanna ga Allah!”