11 Baƙaƙen aljannu kuwa, duk sa'ad da suka gan shi, sai su fāɗi gabansa suna kururuwa, suna cewa, “Kai Ɗan Allah ne.”
12 Sai ya kwaɓe su ƙwarai kada su bayyana shi.
13 Ya hau dutse, ya kira waɗanda yake so, suka je wurinsa.
14 Ya zaɓi mutum goma sha biyu su zauna tare da shi, ya riƙa aikensu suna wa'azi.
15 Ya kuma ba su ikon fitar da aljannu.
16 Ga waɗanda ya zaɓa, Bitrus,
17 da Yakubu ɗan Zabadi, da kuma ɗan'uwansa Yahaya, ya sa musu suna Buwanarjis, wato 'ya'yan tsawa.