2 Sai ya koya musu abubuwa da yawa da misalai. A cikin koyarwa tasa har ya ce musu,
3 “Ku saurara! Wani mai shuka ya tafi shuka.
4 Yana cikin yafa iri, sai waɗansu ƙwayoyi suka faɗa a hanya, tsuntsaye kuma suka zo suka tsince su.
5 Waɗansu kuma suka faɗa a wuri mai duwatsu inda ba ƙasa da yawa. Nan da nan kuwa suka tsiro saboda rashin zurfin ƙasa.
6 Da rana fa ta ɗaga, sai suka yanƙwane, da yake ba su da saiwa sosai, suka bushe.
7 Waɗansu kuma suka faɗa cikin ƙaya, sai ƙayar ta tashi ta sarƙe su, ba su yi tsaba ba.
8 Waɗansu kuma suka faɗa a ƙasa mai kyau, suka yi yabanya, suka girma, suka yi tsaba, waɗansu riɓi talatin talatin, waɗansu sittin sittin, waɗansu ma har ɗari ɗari.”