49 amma da suka gan shi yana tafiya a kan ruwan, sai suka zaci fatalwa ce, suka yi kururuwa,
50 domin duk sun gan shi, sun kuwa firgita. Sai nan da nan ya yi musu magana ya ce, “Ba kome, ni ne, kada ku ji tsoro.”
51 Sa'an nan ya shiga jirgi wurinsu, iska kuma ta kwanta. Sai mamaki ya kama su ƙwarai,
52 don ba su fahimci al'amarin gurasan nan ba, saboda zuciyarsu ta taurare.
53 Da suka haye, suka isa ƙasar Janisarata, suka ɗaure jirgin a gaɓa.
54 Da fitarsu daga jirgin sai mutane suka shaida shi.
55 Suka gama ƙasar da gudu, suka fara ɗaɗɗauko marasa lafiya a kan shimfiɗunsu zuwa duk inda suka ji yake.