5 Sai ya tambaye su, “Gurasa nawa gare ku?” Suka ce, “Bakwai.”
6 Sai ya umarci taron su zauna a ƙasa. Da ya ɗauki gurasan nan bakwai, ya yi godiya ga Allah, ya gutsuttsura, ya yi ta ba almajiransa su kai wa taron, suka kuwa kakkai musu.
7 Suna kuma da ƙananan kifaye kaɗan. Da ya yi wa Allah godiya, sai ya ce su ma a kai musu.
8 Suka ci, suka ƙoshi, har suka ɗauki ragowar gutsattsarin, cike da manyan kwanduna bakwai.
9 Mutanen kuwa sun yi wajen dubu huɗu. Sai ya sallame su.
10 Nan da nan kuwa ya shiga jirgi da almajiransa, ya tafi ƙasar Dalmanuta.
11 Farisiyawa suka zo suka fara muhawara da shi, suna nema ya nuna musu wata alama daga sama, don su gwada shi.