7 Suna kuma da ƙananan kifaye kaɗan. Da ya yi wa Allah godiya, sai ya ce su ma a kai musu.
8 Suka ci, suka ƙoshi, har suka ɗauki ragowar gutsattsarin, cike da manyan kwanduna bakwai.
9 Mutanen kuwa sun yi wajen dubu huɗu. Sai ya sallame su.
10 Nan da nan kuwa ya shiga jirgi da almajiransa, ya tafi ƙasar Dalmanuta.
11 Farisiyawa suka zo suka fara muhawara da shi, suna nema ya nuna musu wata alama daga sama, don su gwada shi.
12 Sai ya yi wata doguwar ajiyar zuciya, ya ce, “Don me mutanen zamanin nan suke neman ganin alama? Hakika, ina gaya muku, ba wata alamar da za a nuna wa mutanen wannan zamani.”
13 Daga nan ya bar su, ya sāke shiga jirgi, ya haye wancan ƙetaren.