7 Sai Yesu ya zo ya taɓa su, ya ce, “Ku tashi, kada ku ji tsoro.”
8 Da suka ɗaga kai ba su ga kowa ba, sai Yesu kaɗai.
9 Suna cikin gangarowa daga dutsen, sai Yesu ya kwaɓe su ya ce, “Kada ku gaya wa kowa abin da kuka gani, sai an ta da Ɗan Mutum daga matattu.”
10 Almajiran suka tambaye shi suka ce, “To, yaya malaman Attaura suke cewa, lalle ne Iliya ya riga zuwa?”
11 Ya amsa ya ce, “Lalle Iliya zai zo ne, zai kuwa raya dukan abubuwa.
12 Amma ina gaya muku, Iliya ya riga ya zo, ba su kuwa san shi ne ba, har ma suka yi masa abin da suka ga dama. Haka kuma Ɗan Mutum zai sha wuya a hannunsu.”
13 Sa'an nan ne almajiran suka gane, ashe, zancen Yahaya Maibaftisma yake yi musu.