17 To, faɗa mana abin da ka gani. Shin, daidai ne mu biya Kaisar haraji, ko kuwa?”
18 Yesu kuwa domin ya gane muguntarsu, sai ya ce musu, “Don me kuke jarraba ni? Ku munafukai!
19 Ku nuna mini kuɗin harajin.” Sai suka kawo masa dinari.
20 Yesu ya ce musu, “Surar nan da sunan nan na wane ne?”
21 Suka ce, “Na Kaisar ne.” Sa'an nan ya ce musu, “To, sai ku ba Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba Allah abin da yake na Allah.”
22 Da suka ji haka, sai suka yi mamaki, suka rabu da shi, suka yi tafiyarsu.
23 A ran nan sai waɗansu Sadukiyawa (su da suke cewa, ba tashin matattu) suka zo wurinsa, suka yi masa tambaya,