18 In mai yiwuwa ne, a gare ku, ku yi zaman lafiya da kowa.
19 Ya ku ƙaunatattuna, kada ku ku yi ramuwa, sai dai ku bar wa fushin Allah. Domin a rubuce yake cewa, “Ramuwa tawa ce, ni zan saka, in ji Ubangiji.”
20 Har ma “in maƙiyinka yana jin yunwa, sai ka ci da shi. In yana jin ƙishirwa, ka shayar da shi. Don ta haka ne za ka tula garwashin wuta a kansa.”
21 Kada mugunta ta rinjaye ku, amma ku rinjayi mugunta da nagarta.