17 Domin wannan uba yake ƙaunata, domin ina ba da raina in ɗauko shi kuma.
18 Ba mai karɓe mini rai, don kaina nake ba da shi. Ina da ikon ba da shi, ina da ikon ɗauko shi kuma. Na karɓo wannan umarni ne daga wurin Ubana.”
19 Saboda maganan nan fa, sai rabuwa ta sāke shiga tsakanin Yahudawa.
20 Da yawa daga cikinsu suka ce, “Ai, mai iska ne, haukansa kawai yake yi. Don me za ku saurare shi?”
21 Waɗansu kuwa suka ce, “A'a, wannan magana, ai, ba ta mai iska ba ce. Ashe, iska tana iya buɗe wa makaho ido?”
22 Lokacin idin tsarkakewa ne kuwa a Urushalima,
23 damuna ce kuma, Yesu kuwa na zagawa a Shirayin Sulemanu cikin Haikali,