12 Sai almajiran suka ce masa, “Ya Ubangiji, in dai barci ne ya ɗauke shi, ai, zai warke.”
13 Alhali kuwa, Yesu zancen mutuwar Li'azaru yake, amma su sun ɗauka yana nufin barcin hutawa ne.
14 Sai Yesu ya gaya musu a fili, ya ce, “Li'azaru dai ya mutu.
15 Ina kuwa farin ciki da ba na nan, saboda ku domin ku ba da gaskiya. Amma mu dai je wurinsa.”
16 Sai Toma, wanda ake kira Ɗan Tagwai, ya ce wa 'yan'uwansa almajirai, “Mu ma mu tafi, mu mutu tare da shi.”
17 Da Yesu ya isa, ya tarar Li'azaru, har ya kwana huɗu a kabari.
18 Betanya kuwa kusa da Urushalima take, misalin mil biyu.