22 Ko yanzu ma na sani kome ka roƙi Allah zai yi maka.”
23 Yesu ya ce mata, “Ɗan'uwanki zai tashi.”
24 Marta ta ce masa, “Na sani zai tashi a tashin matattu a ranar ƙarshe.”
25 Yesu ya ce mata, “Ai, ni ne tashin matattu, ni ne kuma rai. Wanda ya gaskata da ni, ko ya mutu zai rayu.
26 Wanda kuwa yake raye, yake kuma gaskatawa da ni, ba zai mutu ba har abada. Kin gaskata wannan?”
27 Ta ce masa, “I, ya Ubangiji. Na gaskata kai ne Almasihu, Ɗan Allah, shi wannan mai zuwa duniya.”
28 Da ta faɗi haka, ta je ta kirawo 'yar'uwa tata Maryamu, ta raɗa mata ta ce, “Ga Malam ya zo, yana kiranki.”