15 Ba na roƙonka ka ɗauke su daga duniya, sai dai ka kāre su daga Mugun nan.
16 Su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ma ba na duniya ba ne.
17 Ka tsarkake su cikin gaskiya. Maganarka ita ce gaskiya.
18 Kamar yadda ka aiko ni duniya, haka ni ma na aike su duniya.
19 Saboda su ne nake miƙa kaina, domin su ma a tsarkake su cikin gaskiya.
20 “Ba kuwa waɗannan kaɗai nake roƙa wa ba, har ma masu gaskatawa da ni ta maganarsu,
21 domin dukansu su zama ɗaya, kamar yadda kai, ya Uba, kake cikina, ni kuma nake cikinka, haka su ma su kasance cikinmu, domin duniya ta gaskata, cewa kai ne ka aiko ni.