26 Yesu ya ce mata, “Ni ne, ni mai maganan nan da yake.”
27 Nan take almajiransa suka dawo. Suka yi mamakin ganin yana magana da mace. Amma kuwa ba wanda ya ce, “Me kike bukata?” ko, “Don me kake magana da ita?”
28 Sai matar ta bar tulunta, ta koma gari, ta ce wa mutane,
29 “Ku zo, ku ga mutumin da ya gaya mini duk abin da na taɓa yi! Shin, ko wannan shi ne Almasihu?”
30 Sai suka fito daga garin suka nufo shi.
31 Ana cikin haka sai almajiran suka roƙe shi suka ce, “Ya shugaba, ci abinci.”
32 Amma ya ce musu, “Ina da abincin da ba ku sani ba.”