44 Ba mai iya zuwa wurina, sai dai in Uba wanda ya aiko ni ne ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a ranar ƙarshe.
45 A rubuce yake cikin littattafan annabawa cewa, ‘Dukkansu Allah ne zai koya musu.’ To, duk wanda ya ji, ya kuma koya wurin Uba, zai zo gare ni.
46 Ba wai don wani ya taɓa ganin Uban, sai shi wanda yake daga wurin Allah, shi ne ya ga Uban.
47 Lalle hakika ina gaya muku, wanda ya ba da gaskiya, yana da rai madawwami.
48 Ni ne Gurasa mai ba da rai.
49 Kakannin kakanninku sun ci manna a jeji, amma kuwa sun mutu.
50 Ga Gurasa mai saukowa daga Sama, domin kowa yă ci, kada ya mutu.