33 Da mutumin nan ba daga Allah ya fito ba, da ba abin da zai iya yi.”
34 Suka amsa masa suka ce, “Kai da aka haifa a baƙin zunubi ne za ka koya mana?” Sai suka kore shi.
35 Yesu ya ji labari sun kore shi. Da ya same shi, ya ce, “Ka gaskata da Ɗan Mutum ko?”
36 Ya amsa ya ce, “Wane ne shi, ya Shugaba, da zan gaskata da shi?”
37 Yesu ya ce masa, “Ai, ka gan shi, shi ne ma mai magana da kai.”
38 Sai ya ce, “Ya Ubangiji, na ba da gaskiya,” ya kuma yi masa sujada.
39 Yesu ya ce, “Na shigo duniyan nan ne don rarrabewa, domin waɗanda ba sa gani su gani, waɗanda suke gani kuma su makance.”