1 Sa'ad da Dawuda yake zaune a fādarsa, sai ya ce, wa annabi Natan, “Ga shi, ni ina zaune a cikin gidan da aka yi da itacen al'ul, amma akwatin alkawarin Ubangiji yana cikin alfarwa.”
2 Natan ya amsa masa ya ce, “Ka yi duk abin da zuciyarka ta ɗauka, gama Allah yana tare da kai.”
3 Amma a wannan dare Ubangiji ya yi magana da Natan, ya ce,
4 “Ka tafi, ka faɗa wa bawana, Dawuda, cewa ni Ubangiji na ce, ‘Ba za ka gina mini ɗakin da zan zauna a ciki ba.
5 Gama tun ranar da na fito da Isra'ilawa ban taɓa zama a cikin ɗaki ba, amma daga alfarwa zuwa alfarwa, daga wannan mazauni kuma zuwa wancan.
6 A dukan wuraren da na tafi tare da Isra'ilawa, ban taɓa faɗa wa wani daga cikin hakiman Isra'ila, waɗanda na ba da umarni su yi kiwon jama'ata, cewa su gina mini ɗaki da itacen al'ul ba.’