4 “Tsohonka ya tsananta mana, yanzu sai ka sawwaƙa mana irin tsananin da muka sha daga wurin tsohonka, da irin tilastawar da ya yi mana, sa'an nan sai mu bauta maka.”
5 Rehobowam kuwa ya ce musu, “Ku komo bayan kwana uku.” Sai jama'a suka tafi.
6 Rehobowam ya nemi shawara a gun dattawan da suke tare da tsohonsa Sulemanu, sa'ad da yake da rai, ya ce, “Wace shawara za ku ba ni don in amsa wa jama'ar nan?”
7 Su kuwa suka ce masa, “Idan za ka nuna wa jama'ar nan alheri, ka daɗaɗa musu rai, ka kuma yi musu magana mai daɗi, za su zama barorinka har abada.”
8 Amma ya ƙi yarda da shawarar da dattawan suka ba shi, ya nemi shawara daga wurin matasa waɗanda suka girma tare, masu yi masa hidima.
9 Ya ce musu, “Wace irin shawara za ku bayar wadda za mu amsa wa jama'an nan da suka ce mini, ‘Ka sawwaƙa mana wahalar da muka sha daga wurin tsohonka’?”
10 Sai matasa waɗanda suka girma tare da shi, suka ce masa, “Ga abin da za ka faɗa wa jama'an nan da suka ce maka, tsohonka ya tsananta musu, yanzu sai ka sawwaƙa musu, ‘Ƙaramin yatsana ya fi ƙugun ubana kauri!