29 Sarkin Isra'ila ya ce wa Yehoshafat, “Zan ɓad da kama, in shiga yaƙi, amma kai, sai ka sa rigunanka.” Sarkin Isra'ila kuwa ya ɓad da kama, suka shiga yaƙi.
30 Sarkin Suriya ya umarci shugabannin karusansa, ya ce, “Kada ku yi yaƙi da yaro ko babba, sai dai da Sarkin Isra'ila, shi kaɗai.”
31 Sa'ad da shugabannin karusai suka ga Yehoshafat, suka ce, “Wannan ne Sarkin Isra'ila,” sai suka juya suka yi yaƙi da shi. Amma Yehoshafat ya yi kururuwa, Ubangiji Allah ya kuɓutar da shi, Allah kuwa ya kawar da su daga gare shi.
32 Da shugabannin karusai suka ga, ashe, ba Sarkin Isra'ila ba ne, sai suka daina binsa suka juyo.
33 Amma wani mutum ya harba kibiya haka kawai, ya sami Sarkin Isra'ila a mahaɗin kafaɗa. Sai sarkin ya ce wa wanda yake korar karusarsa, “Juya ka fitar da ni daga wurin yaƙin, gama an yi mini rauni.”
34 Ran nan yaƙin ya tsananta, Sarkin Isra'ila kuma ya jingina a cikin karusarsa, yana fuskantar Suriyawa har maraice, rana na fāɗuwa yana rasuwa.